1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: An sake yin garkuwa da dalibai

June 17, 2021

Wasu yan ta'adda da ba a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da dalibai mata a jihar Kebbi.

https://p.dw.com/p/3v7qO
Nigeria Katsina | Kankara | Angriff auf Schule
Hoto: Abdullahi Inuwa/REUTERS

'Yan bingiga sun sake yin awon gaba da yara mata yan makaranta da ba a tantance adadinsu ba kawo yanzu a wata kwalejin gwamnatin tarayya da ke garin Yauri na jihar Kebbi arewa maso yammacin Najeriya, kwanaki kalilan bayan sace wasu daliban a garin Kwantagora mai makwabtaka da birnin na Yauri.

Gabanin sace yan makarantar da malamansu guda uku, sai da yan bindigar suka hallaka wani jami'in dan sanda daya yayin da su ke musayar wuta da barayin ta bakin mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar Nafiu Abubakar.

Haka zalika a jihar Ogun da ke kudu maso yammacin kasar ma masu garkuwa da mutane sun dauke wasu 'yan China hudu ma'aikatan layin dogo bayan hallaka jami'in dan sandan da ke gadinsu.