1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Halin rayuwar 'yan gudun hijira

Abdourahamane Hassane
October 11, 2017

Wata kungiya ta kasar Norway NRC ta ce wadanda yakin Boko Haram ya rutsa da su a yanki arewa maso gabashin Najeriya za a kwashe lokaci mai tsawo kusan gomai na shekaru suna bukatar agajin kasashen duniya.

https://p.dw.com/p/2lfp4
Nigeria UN Camp in Maiduguri
Hoto: picture alliance/dpa/AP/S. Alamba

A cikin wani rahoton da kungiyar ta NRC ta bayyana,ta ce a binciken da ta gudanar cikin wadanda suka fice daga gidajensu kusan mtum dubu 27 cikin miliyan daya da rabi. Kishi 86 cikin dari sun ce ba a shirye suke ba su sake koma a matsugunasu saboda abin da suka kira har yanzu na rashin tabbas a kan sha'anin tsaro.