1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta amince da kananan matatun Mai

August 4, 2017

Fadar shugaban kasa a Najeriya, ta ce gwamnati za ta halalta kananan matatun mai na 'yan ganima a yankin Niger Delta da ke kudancin kasar, inda za a rika sayar masu da danyen mai cikin sauki don su rika tacewa.

https://p.dw.com/p/2hhuB
Nigeria Bodo, Ogoniland Öl
Hoto: AP

A cewar gwamnatin Najeriyar za a fara hakan ne a karshen shekarar da ake ciki, kamar yadda shugabannin yankin na Niger Delta suka bukata. A ranar Litinin da ta gabata ne dai jagabannin yankin Niger Delta, suka yi barazanar janyewa daga tattaunawar sulhu da gwamnatin Najeriyar, muddin aka ki amince wa bukatunsu nan da ranar 1 da watan Nuwamba.

Yanzu dai gwamnatin za ta samarwa kowacce daga cikin jihohin yankin mai arzikin mai, kananan matatu biyu-biyu wadanda za su fara harkar tace man da su. Akwai ma tattaunawar da ake kai da manyan kamfanonin irinsu Shell da Chevron, don su kafa manyan cibiyoyinsu a yankin na Niger Delta.

Amincewa hakan dai, na daga cikin dabaru ne na maganta fashe bututun mai da ke faruwa a yankin da mazauna ke cewa ba sa samun amfanin arzikin da ke a yankin na su.