1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta nemi hadin gwiwar Makwabtanta

February 26, 2014

Ministan harkokin yada labaru Labaran Maku, ya jaddada bukatar agajin makwabtan Najeriyar, musamman renon Faransa wajen kawo karshen rikicin Boko Haram.

https://p.dw.com/p/1BFPh
Unruhe und Gewalt in Nigeria ARCHIVBILD
Hoto: Pius Utomi Ekpei/AFP/Getty Images

Najeriya ta yi kira ga makwabtan a, kasashe renon Faransa na Afirka ta Yamma, musamman ma kasar Kamarun, da su dafa a kokarin magance matsalar Boko Haram tun kafin su fara kai ga muradu na Faransa.

Da yake magana Ministan yada labaru na kasar ta Najeriya Labaran Maku, ya ce "ni a ganina, ya kyautu mu hada karfi da karshe da faransawa, da kasashen dake anfani da harshen faransanci na Afirka ta yamma, muddin dai ana so a magance wannan matsala."

Wannan kira ya zo ne 'yan sa'o'i kadan kafin ziyarar da shugaban kasar Faransa François Hollande, zai kai a kasar ta Tarayyar Najeria a wannan Alhamis (27.02.14), wanda zai kasance babban bako mai alfarma a bukin zagayowar hadewar kasar a matsayin dunkulallar kasa.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Zainab Mohammed Abubakar