1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Za a tuhumi Obasanjo kan kudin lantarki

May 23, 2018

Shugaba Muhammadu Buhari ya nemi a binciki tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo kan badakalar kudi na dalar Amirka Miliyan dubu 16 da aka kebe don samarwa jama’a wuta lantarki a yayin mulkinsa.

https://p.dw.com/p/2yC3t
Nigeria Abuja - President Muhammadu Buhari und ehemaliger Präsident Olusegun Obasanjo
Hoto: picture-alliance/NurPhoto/next24online

 A baya sun hada kai da nufin tabbatar da kare mulkin ‘yan lema ta PDP a Najeriya, to amma kuma akwai alamar raba gari a tsakanin tsofaffin abokan takun guda biyu. Babu dai zato ba kuma tsamanni, shugaban da ke mulki  ya zargi  Obasanjo da watsar da tsabar kudi har dalar Amirka Miliyan dubu 16 amma kuma ba tare da yin tasiri a cikin masana'antar wutar kasar ba, lamarin da ya auku a lokacin da tsohon shugaban ke kan madafun iko.

Afrika Elektrizität Nigeria Afam VI
Hoto: Getty Images/AFP/F. Plaucheur

Abun kuma da ya harzuka tsohon  shugaban da ya dora karatun jahilci ga Buharin tare da kalubalantarsa zuwa ga binciken batun. Ana dai kallon sabon rikici na abokan kuma duk tsofaffin janar janar na sojan a matsayin wani nau'i na siyasar da ake shirin gani cikin kasar anan gaba.

Tuni dai Obasanjon yai nisa a kokari na kare mulkin na Buhari tare da zaman babban jigo na masu adawar cikin kasar a halin yanzu. Abun jira a gani dai na zaman yadda take shirin da ta kaya ga fage na siyasar dake niyyar tura daya a cikin tsofaffin janar janar na sojan ya zuwa gidan tarihi na siyasa.