1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nasarar dakile cutar Ebola a Kwango

Lateefa Mustapha Ja'afarNovember 15, 2014

Mahukunta a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango sun tabbatar da cewa babu cutar Ebola a kasar.

https://p.dw.com/p/1Do2N
Hoto: picture alliance/AP Photo

Ministan lafiya na kasar Felix Kabange Numbi ne ya ba da wannan tabbacin inda ya ce a yanzu babu kwayar cutar kwata-kwata a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango. A watan Agustan da ya gabata ne dai kwayar cutar Ebola ta bulla a kasar da ke yankin Tsakiyar Afirka, inda ta lakume rayuka 49. Sai dai jami'an kiwon lafiya sun bayyana cewa Ebolan da ta bulla a Kwango na da ban-banci da kwayar Ebolan da ta bulla a yankin yammacin Afirka wadda kawo yanzu ta yi sanadiyyar rayukan mutane 5,100 a wannan yanki.