1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: An kammala yakin neman zabe

Ahmed SalisuFebruary 20, 2016

A cikin daren jiya Juma'a ce aka kawo karshen yakin neman zabe na shugaban kasa da na 'yan majalisar dokoki da yi a gobe Lahadi.

https://p.dw.com/p/1Hz4p
Niger Sympathisanten des früheren Parlamentspräsidenten Hama Amadou
Hoto: DW/D. Köpp

Hankula al'ummar kasar dai yanzu haka ya karakata kan yadda wannan zabe zai gudana wanda shugaban kasar Mahamadou Isoufou zai fafata da 'yan takara 14 ciki kuwa har da Hama Amadou na jam'iyyar Moden Lumana Afirka wanda yanzu haka ke tsare a gidan kaso.

A bangaren 'yan majalisu kuwa, kimanin 'yan takara 5,200 ne daga jami'yyu daban-daban na kasar ke zawarcin kujeru 171 da ake da su a zauren majalisar dokokin kasar. Batun tsaro da dakile tashin hankali yayin zaben dai na daga cikin abubuwan da jami'an tsaro suka sanya a gaba a zaben na Nijar na bana.