1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Shirin zaben gama-gari

Salissou Boukari AdamouJanuary 21, 2016

Bayan tabbatar da jerin sunayan 'yan takarar shugabancin kasa a Jamhuiriyar Nijar, hukumar zaben kasar CENI ta sanar da soma rarraba katunan zabe a fadin kasar.

https://p.dw.com/p/1Hhf2
Sudan Wahlen
Hoto: AFP/Getty Images/P. Baz

A ranar 21 ga watan Febrairu na 2016 ne za a gudanar da zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisun dokoki a Jamhuriyar Nijar, wanda kotun tsarin mulkin kasar ta amince da takardun 'yan takara 15 daga cikin 16 da aka gabatar a gabanta. Hakan ya nunar cewa 'yan takara 15 ne za su fafata a zaben na shugaban kasa. Sai dai kuma daya daga cikinsu Hama Amadou na jam'iyyar Moden FA Lumana Afrika, na ci gaba da zama a gidan yari na garin Fillingue da ke a nisan kilomita kusan 200 da Yamai babban birnin kasar.