1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Obama zai gana da 'yan majalisar dokoki

October 2, 2013

Shugaban Amurka Barack Obama zai tattauna da jiga-jigan majalisar dokokin kasar kan kiki-kakar da ake tsakanin majalisar wakilai da gwamnati kan kasafin kudi.

https://p.dw.com/p/19t38
President Barack Obama pauses before a speaking about the ongoing budget battle from the Brady Press Briefing Room at the White House in Washington, Monday, Sept. 30, 2013. Obama is ramping up pressure on Republicans to avoid a post-midnight government shutdown. He says a shutdown would hurt the economy and hundreds of thousands of government workers. (AP Photo/Susan Walsh)
Shugaban Amurka Barack ObamaHoto: picture-alliance/AP Photo

Nan gaba kadan ne shugaban Amurka Barack Obama zai yi wata ganawa da kakakin majalisar wakilai John Boehner da Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa Harry Reid gami da Nancy Pelocy da kuma Mitch McConnell da ke zaman shugabannin marasa rinjaye a majalisar wakilai da ta dattawa.

Yayin wannan gawana dai wadda za a soma ta da misalin karfe tara da rabi agogon GMT, ana sa ran Obama zai yi kokarin lallabar 'yan majalisar da su sassauto daga matsayin da suka dauka kan kasafin kudi wanda ya sanya dakatar da aiyyukan hukumomi da ma'aikatun gwamnatin kasar saboda rashin kudin tafiyar da su.

Kazalika rahotanni daga fadar mulki ta White House na cewar shugaban na Amurka zai yi amfani da taron wajen jan hankalin 'yan majalisar da su amince da wani kuduri da zai kara mizanin bashin da gwamnati za ta ci don kauracewa gaza samun kudaden tafiyar da gwamnati.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammed Awal Balarabe