Omar Al-Bachir ya gana da Salva Kiir
January 5, 2013
Shugaba Omar Hassan El-Bechir na Sudan ya gana da takwaransa Salva Kir na Sudan ta Kudu a birnin Adis Ababa na habasha a wannan Asabar,inda suka maida hankali ga batun rikicin kan iyakar da ke tsakanin kasashen nasu guda biyu. Ana dai tautaunawar ne a karkashin jagorancin kungiyar tarayyar Afrika wato AU.
Tun can farko saida shugaba Al-Bechir ya gana da sabon Praministan Ethiopian Hailemariam,da kuma mai shiga tsakani a rikicin kasashen tsohon shugaban kasasr Afrika ta Kudu Thabon Mbeki.
Wannan tautaunawar na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Sudan ta Kudu ke zargin Khartum da aika dakarunta domin kai hari a kudancin Sudan musamman a garin Bahr-El Ghazal,inda rahotani suka bayana mutuwar a kalla fararen fula 3 zargin da Khartum ta musanta.
Dama a can baya kasashen biyu sun cimma wata yarjejeniyar ci-gaba da tono man fetur da ke Sudan ta Kudu,yarjejeniyar da babu bangaren da ya mutuntata.
Mawallafi: Issoufou Mamane
Edita: Usman Shehu Usman