1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Pakistan ta zargi Amirka da katsalandan

November 3, 2013

Bayan da Amirka ta kai harin da ya hallaka shugaban Taliban Hakimullah Mehsud ba tare da izininta ba, gwamnatin Pakistan ta ce Amirka na yi mata shisshigi a harkokinta na tsaro.

https://p.dw.com/p/1AAq7
People burn a mock US flag as they shout slogans during a protest against US drone attacks, in Multan, Pakistan, 24 January 2012. At least five alleged militants were killed on 23 January by a US unmanned aircraft in north-western Pakistan, intelligence officials said. The attack hit a compound and one vehicle in the village of Degan in the Data Khel area near Miransha, the main town in North Waziristan, an intelligence official said on condition of anonymity. EPA/MK CHAUDHRY +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Gwamnatin Pakistan ta zargi takwararta ta Amirka da haifar da tafiyar hawainiya a yunkurin da take yi na sulhunta rikicin da ke tsakaninta da masu kaifin kishin addini na kungiyar Taliban. Wannan kuwa ya faru ne bayan da ita Amirka ta yi amfani da jirage maras matuka wajen kashe jagoran kungiyar Taliban Hakimullah Mehsud, kwana guda kafin kaddamar da taron zaman lafiya tsakanin sassan biyu.

Fadar mulki ta Islamabad ta gayyaci Jakadan Amirka a kasarta inda ta bayyana masa rashin jin dadin gwamnati game abin da ta danganta da shisshigin da Amirka ke yi mata a harkokinta na cikin gida. Ministan watsa labaran wannan kasa Pervez Rashid ya ce wannan kisan ba karamin dagula wa gwamnati lissafi ya yi ba a kokarin da take na cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Taliban ba.

Tuni ma dai jami'an tsaron kasar ta Pakistan suka shiga cikin shirin ko ta kwana bayan kashe jagoran kungiyar Taliban Hakimullah Mehsud da kuma nada Sayed Khan a matsayin sabon jagora.

Mawallafi: Mouhamadou Awal Balarabe
Edita: Saleh Umar Saleh