1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka ta Kudu: Kalubalen Ramaphosa

Usman Shehu Usman
May 25, 2019

Akalla mutane dubu 35 ne suka hallara a bikin rantsar da  Cyril Ramaphosa a matsayin shugaban kasar Afirka ta Kudu

https://p.dw.com/p/3J40q
Südafrika Pretoria | Amtseinführung Cyril Ramaphosa, Präsident
Hoto: Reuters/S. Sibeko

Sabon shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya yi rantsuwar kama aikin ne a gaban shugabannin gwamnatocin kasashen Afirka da dama. Bikin rantsuwar wanda ya gudana a Pretoria babban birnin kasar, an shirya 'yan sanda dubu 25 don tabbatar da tsaro.

A cewa  Khusela Diko kakakin shugaban kasar, a lokacin kama rantsuwa Shugaba Cyril Ramaphosa zai tabo batun hadin kan kasa da samarwa matasa aikin yi da kuma farfado da martabar kasar a matsayin wacce ke fada a ji a harkokin nahiyar Afirka. Mai shekaru 66 a duniya, Ramaphosa  ya kasance mataimakin shugaba Jacob Zuma tun a shekara ta 2014, sai dai akwai babban kalubale da ke jiransa musamman rashin aikin yi da kuma yakar cin hanci da rashawa.