1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana shirye-shiryen rantsar da sabuwar majalisar a Najeriya.

Kamaluddeen SaniNovember 11, 2015

A ranar larabar nan ce shugaban tarayyar Najeriyar Muhammadu Buhari zai rantsar da sabuwar majalisar ministocin kasar bayan jiran tsawon watanni biyar.

https://p.dw.com/p/1H3kx
Muhammadu Buhari Präsident Nigeria Porträt G7 Gipfel 2015 Schloss Elmau
Hoto: picture-alliance/dpa/Minkoff

Ana san ran cewar nan ba da jimawa bane shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya zai bada sanarwar kafa sabuwar majalisar zartawar kasar da ke jagaba ta fuskar tattalin arzikin kasa a nahiyar Afrika.

Bikin rantsarwar dai zai gudana ne a farfajiyar Aso Rock dake a Abuja fadar gwamnatin Najeriyan.

Ministocin dai sun hada da kwarraru daga fagage da dama na cigaban jama'a da mafiya yawan 'yan Najeriya suke ma kallon ko shakka babu kwaliya zata biya kudin sabulu.