1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

China da Rasha na kawo cikas ga G20

Abdourahamane Hassane
March 2, 2023

Ministocin harkokin waje na kasashe masu arzikin masana'ntu na shirin ganawa a yau a birnin New Delhi na Indiya a cikin rarrabuwar kawunan kan yakin Ukraine.

https://p.dw.com/p/4O95V
Indien G20-Treffen in Delhi
Hoto: India's Ministry of External Affairs/Handout/REUTERS

Tuni da jagoran diflomasiyyar Amirka Antony Blinken da ake sa ran zai halarci taron,ya yi gargadin cewar ba zai gana ba da takwaransa na Rasha Sergei Lavrov a wannan ganawar ta kwanaki biyu tsakanin ministocin harkokin wajen na G20. A ranar Asabar, taron ministocin kudi na G20 an waste hannun riga saboda China da Rasha sun ki amincewa su saka hannu a kan sanarwar bai daya ta karshen taron.