1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin amicewa da sojojin Farasana a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

August 21, 2014

Dubban jama'a suka gudanar da gangami a birnin Bangui domin neman ganin sojojin Faransa sun fice daga ƙasar.

https://p.dw.com/p/1Cyxu
Zentralafrikanische Republik
Hoto: Getty Images/AFP/Pacome Pabandji

Masu aiko da rahotannin sun ce duk da ruwan sama kamar da bakin Ƙwarya da aka riƙa yi a birin, jama'ar sun yi jerin gwano tun daga anguwar PK5 har zuwa cibiyar rundunar sojojin kiyaye zaman lafiya ta MDD wato MUNISCA.

Suna raira kallamun suka ga shugaba Francois Hollande saboda zargin da suke yi wa sojojin na Faransa da galazawa musulmi. Wannan gamgami ya biyo bayan wata arangama da aka sha a kwanaki biyun da suka wuce, tsakanin musulmin da sojojin na Faransar waɗanda ke ƙoƙarin ƙwace makamai daga hannu jama'a .

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe