1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin isassun kudaden yaki da yunwa a Sudan ta Kudu

Mohammad Nasiru AwalFebruary 10, 2016

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ba ta da kudin yaki da matsananciyar yunwa da ke barazana ga miliyoyin mutane a Sudan ta Kudu.

https://p.dw.com/p/1HshN
Dürre in Angola Bevölkerung
Hoto: DW/A.Vieira

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kaso kadan take da shi na yawan kudaden da take bukata wajen yaki da barazanar matsalar yunwa a Sudan ta Kudu. Mai kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Sudan ta Kudu Eugene Owusu ya ce ya zuwa yanzu kashi biyu cikin 100 na dala miliyan dubu 1.3 da suke bukata kawai suka samu. Mutane kimanin miliyan 2.8 a kasar wadda tun a karshen shekarar 2013 ta tsunduma cikin yakin basasa, ke bukatar taimakon abinci cikin gaggawa. Akalla mutane dubu 40 a cikinsu na fuskantar barazanar matsananciyar yunwa. Jami'in ya ce ana bukatar tura kayan abinci cikin gaggawa zuwa yankunan kasar da tun faduwar damina a cikin watan Yuni ke da wahalar kaiwa saboda rashin hanyoyi masu kyau.