1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikice-rikice ka iya rusa Masar

January 29, 2013

Babban habsan sojan ƙasar Masar ya yi gargadin cewa rikice-rikicen siyasan da ƙasar ke fuskanta ka iya durƙusar da ita baki daya

https://p.dw.com/p/17TnD
Egyptian protesters clash with riot police near Cairo?s Tahrir Square on January 28, 2013. Egypt's main opposition bloc rejected an invitation by President Mohamed Morsi for talks on the violence and political turmoil sweeping the country and instead called for fresh mass demonstrations. AFP PHOTO / KHALED DESOUKI (Photo credit should read KHALED DESOUKI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images

A wannan Talata, babban habsan sojan ƙasar Masar ya yi gargadin cewa rikice-rikicen siyasan da ƙasar ke fuskanta ka iya durƙusar da ita baki daya. Wannan yayin da dubban mutane su ka yi fatali da dokar hana fita da aka kafa cikin wasu birane, kuma mutane kimanin 52 su ka hallaka kawo yanzu.

Janar Abdel Fattah al-Sissi wanda kuma shi ne ministan tsaro, ya ce, tashin hankalin da ƙasar ke fuskanta na siyasa da tattalin arziki za su iya wargaza ƙasar da kuma barazana da al'uma ta gaba ɗaya.

Cikin ƙarshen mako Shugaban ƙasar ta Masar Mohamed Mursi ya aiyana dokar ta ɓaci cikin birane uku na Port Said, Ismailiya da Suez. Kuma ranar Litinin Majalisar Dattawa ta amince da matakin. Amma mutane na ci gaba da bijirewa dokar cikin waɗannan birane.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Yahouza Sadissou Madobi