1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin jam'iyyar PDP ya ki ci ya ki cinyewa

Abdul-raheem HassanAugust 18, 2016

Mabanbantan hukuncin kotuna da ake ci gaba da samu a Najeriya dangane da takaddamar shugabanci a babbar jam'iyyar adawa ta PDP, yana kara jefa jam'iyyar cikin rudu.

https://p.dw.com/p/1JksE
Karikatur Nigeria PDP Krise
Hoto: DW

Tun bayan da jam'iyyar PDP ta sha kaye a babban zabe da ya gudana a bara, har yanzu jam'iyar da ta shafe shekaru 16 tana shugabancin Najeriya ta gaza dai-daita rikicin cikin gida da ya mamaye ta.

Tun bayan murabus din tsohon shugaban jam'iyyar Adamu Mu'azu, Sen. Ali Modu Sheriff da Sen. Ahmed Makarfi ke ta ja in ja a kan wanda zai dare kan kujerar shugabancin jam'iyyar.