1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Kwango na daukar sabon salo

March 5, 2013

Dubban 'yan kasar ta Kwango ke kauracewa matsugunnensu sakamakon barkewar rikici a dalilin takaddama tsakanin kabilu da neman mallakar albarkatun kasa

https://p.dw.com/p/17r03
epa03474001 Refugees flee the fighting between the rebel M23 forces and forces loyal to the government hear Goma, Eastern Congo DRC, 16 November 2012. A weeks-long ceasefire in the eastern Democratic Republic of Congo appeared to be breaking down 16 November amid reports of troop movements and ongoing fighting between government forces and rebels. Late on 15 November, the M23 rebel group said it had come under attack from government troops and retaliated. Congolese government officials, who say the rebels attacked first, indicated dozens have died in the latest outbreak of violence. Thousands of refugees have fled the massive central African country to neighbouring Rwanda over the past few days, adding to the hundreds of thousands already displaced. Kigali is accused by the UN and Kinshasa of backing the M23 movement, which is largely comprised of ethnic Tutsis, like the Rwandan government. EPA/Alain Wandimoyi
Hoto: picture-alliance/dpa

Ƙungiyoyin agaji sun ce aƙalla muatne 70 suka mutu wasu dubban kuma suka ƙauracewa matsugunnensu bayan da aka shafe kwanaki ana gumurzu tsakanin 'yan tawaye da dakarun gwamnati a gabashin Jamhoriyar demokraɗiyyar Kwango.

Rikicin tsakanin dakarun sojin da 'yan ƙungiyar tawayen APCLS wanda aka fara a makon da ya gabata a garin Kitchanga shine rikicin baya-bayan nan a jerin rikice-rikicen da suka addabi wannan yanki da ke fama da illolin ƙabilanci da taƙaddama kan albarkatun ƙarƙashin ƙasa

Waɗannan rigingimu na nuna irin sarƙaƙiyar da faɗace-faɗacen na gabashin Kwango, musamman ma batun jagoranci da mallakar albarkatun ƙarƙashin ƙasa inda ake zargin dakarun kowani gefe da amfani da miyagun ƙwayoyi da ma fyaɗe da kuma kisan fararen hulan da basu ji basu gani ba.

Mawallafiya: Pinado Abdu Waba
Edita: Mohammed Awal Balarabe