1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mayakan Houthi sun kwace birnin al-Hazm

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 14, 2015

Rahotanni daga kasar Yemen na nuni da cewa mayakan 'yan tawayen Houthi sun kwace iko da al-Hazm babban birnin gundumar al-Jawf.

https://p.dw.com/p/1Fh2F
Yaki ya dai-daita Yemen
Yaki ya dai-daita YemenHoto: picture alliance/Y. Arhab

Kwace birnin na al-Hazm da ke kan iyakar kasar da Saudiya na zuwa ne a dai-dai lokacin da dakarun rundunar taron dangi da Saudiya ke jagoranta ke ci gaba da luguden wuta a kasar a kokarin da take na fatattakar 'yan Houthi. Kwace iko da birnin na al-Hazm dai na zaman wata gagarumar nasara da 'yan tawayen suka samu kwana guda gabanin tattaunawar sulhu da Majalisar Dinkin Duniya ta shirya domin bangarorin da ke yakar juna a Yemen din a birnin Geneva.

Wani mazaunin birnin na al-Hazm ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho cewa: a yanzu haka dakarun Houthi da kuma mayakan da ke goyon bayan tsohon shugaban kasar Ali Abdullah Saleh sun mamaye gine-ginen gwamnati a birnin.