1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Najeriya ya fara sabon wa'adi cike da kalubale

Kamaluddeen Sani Shawai SB
May 29, 2019

An fara sabon wa'adi karkashin kalubale mai tsauri ga Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya da mataimakinsa Ferfesa Yemi Osinbajo a karo na biyu na karin wasu shekaru hudu.

https://p.dw.com/p/3JSHP
Nigerias Präsident Buhari und sein Vize beim APC-Parteitag
Hoto: Novo Isioro

 

Shugaba Muhammadu Buhari da Mataimakin sa Ferfesa Yemi Osinbajo sun yi rantsuwa a dandalin Eagle square a birnin tarayya Abuja a gaban daruruwan mutane ciki harda jami’an diplomasiya na kasashen ketare da kuma jagororin jamiyyar APC mai mulki a Najeriya da tsoffin ministoci da makaraban gwamnati gami da magoya bayan shugaban.

Wannnan dai shi ne karo na biyu da Shugaba Muhammadu Buhari ya sake dawowa madafun iko a Najeriya kasar kuma da ke cike da tarin kalubale kama daga na tsaro, tattalin arziki, rashin aikin yi a tsakanin milyoyin matasa gami da matsalar baya-bayan nan ta yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa na daga cikin batutuwan da shugaban zai tinkara a shekaru hudu da ke tafe.

Mafi yawancin ‘yan Najeriya dai na kallon shugaban a matsayin mai halin dattaku da nuna gaskiya gami da kishin kasarsa kuma mutum ne mara tsoro wajen yaki da cin hanci da karbar rashawa a inda a gefe guda wasu ke kallon gazawar gwamnati wajen daukar matakan da suka dace domin dora kasar a turba ga batun alkawuran da gwamnatin ta dauka a baya.

‘Yan Najeriya sun zuba idanu domin kallon zubin mulkin Shugaba Muhammadu Buhari wa’adi na biyu musamman a bangarorin tsaro da yaki da cin hanci da kuma gyara tattalin arzikin kasar da talawa za su amfana.