Najeriya: Shugabanin al'umma sun damu da rashin tsaro
July 19, 2019A baya dai har an kusan fara bugun kugen fada, kuma wasu ma sun ce suna shirin kare kai, duka bayan wani rikicin sata da kisan al’ummar da ke ruruwa irin ta wutar daji a cikin tarrayar Najeriya. Rikicin da sannu a hankali ke neman rikidewa zuwa rikici na kabilanci dama barazana irin ta kisan kiyashi. Kisan wata 'yar shugaban wata kungiyar kabila mai tasiri a kasar ne dai ya kai ga tada jijiyar wuyan da martani daga manyan sarakuna a yankin Kudancin kasar da suka ce a shirye suke su kare kansu. Bayan wannan yunkurin farkon, za a ce hankula sun soma kwanciya domin su kansu shugabannnin na gano tasirin na zama na lafiya ya dara komawa dan sarki.
Daya daga cikin sarakunan da ke kan gaba a cikin rikicin can baya kuma basarake mafi tasiri na kabilar Yarabawa, Oni Adeyeye Ogunwusi na Ife, ya ce lokaci ya yi na tsaida kugen yakin da amonsa ke yaduwa cikin kasar a halin yanzu tare da bada damar kyale jami’an tsaro aikinsu wajen gano masu laifi. Shugaban kasa dai, ya bai wa hafsoshin tsaro musamman ma shugaban 'yan sanda umarni mai kyau.
Ana dai kallon wani ganawa da aka yi a tsakanin shugaban kasar da babban basarake Oni na Ife, a matsayin kokarin kashe wutar rikicin da ke neman bazuwa zuwa sassa na kasar. Najeriyar dai, ya zuwa yanzu na ji har a tsakar ka sakamakon sauyin yanayin da ya kai ga ta'azarar na talauci sannan kuma ya kara habbaka aikin laifi a kokari na hana abin kai wa bakin salati.