1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakon saki mata ta salula a Saudiyya

Mahmud Yaya Azare AH
January 8, 2019

A Saudiya,wata sabuwar dokar kasar da za ta bai wa mata damar sanin mazajensu sun sakesu, tun kafin su sanarwa alwalinsu ko iyaye da muharammansu na ci gaba da jawo cece-kuce a kasar.

https://p.dw.com/p/3BBj5
Saudi-Arabien 1. Tag Fahrerlaubnis für Frauen
Hoto: Reuters/H. I Mohammed

Daga ranar Lahadin da ta gabata, kotunan kasar za su bukaci mazan aure su aika wa matansu shaidar saki ta hanyar sakon wayar salula, ba tare da sanarwa alwaliyen matan ba, kamar yadda ake yi a da, batun da wasu ke yi wa kallon ci gaba ne na irin 'yanci da sakin mara ga matan kasar ta Saudiya da yarima mai jiran gadon kasar Muhammad Bin Salman ya faro. Mahukuntan na Saudiyya dai sun sha nuna cewar matan kasar sun jima suna shigar da kara a kotunan kasar kan mazajensu da ke sakinsu ba tare da saninsu ba.