1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sharar fage na taron kolin Yankin Gabas ta Tsakiya

Ibrahim SaniNovember 19, 2007
https://p.dw.com/p/CIlU

A nan gaba a yau, Faraminista Ehud Olmert na Israela da takwaransa na Falasɗinawa Mahmud Abbas, za su gana a game da rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya.Ganawar ta yau dai za ta kasance ta ƙarshene, kafin taron ƙolin Yankin Gabas ta Tsakiya da Amirka ke shirin gudanarwa. Amirkan na shirin gudanar da taron ne, a Jihar Maryland dake ƙasar a ranar 27 ga watannan da muke ciki.Taron zai mayar da hankaline wajen samo bakin zaren warware rikicin Yankin Gabas ta tsakiyan, musanmamma, a tsakanin Israela da Falasɗinawa.