A cikin shirin bayan labaran duniya za ku ji DW ta yi waiwaye adon tafiya kan yadda gwamnatin jam’iyyar PNDS Tarayya ta riki ‘yancin dan adam a Nijar, yayin da ake tunkarar zaben shugaban kasa. Gwamnan jihar Bornon Najeriya kuma ya gana da ‘yan gudun hijira a kasar Chadi. A Kamaru kuma an dakatar da kungiyar likitoci ta Doctors without borders a yankin Bamenda.