Talla
Alaka tsakanin masarautun gargajiya na Afrika da mafarauta, alakace da ta samo asali tun iyaye da kakanni, domin kai ana iya cewa mafarauta ne suka kafa garuruwa da dama a yayin tafiye-tafiyensu na harbi. Birnin Zinder da ake kira Damagaram na daga cikin manyan masaurantun gargajiya masu dumbun tarihi a jamhuriyar Nijar kuma mafarauta suka kafa shi shekaru da dama da suka gabata kafin zuwan sakin farko Malam Yunus a 1731. Domin martaba wannan al'ada da ke zaman ginshiki a tarihin birnin na Damagaram an shirya wata kasaitattar haduwar ''Maharban Afrika'' wacce aka yi wa taken ''Festival international des Chasseurs''.