1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Buhari ya kai ziyara jihar Borno bayan harin 'yan ta'adda

February 12, 2020

Shugaba Buhari ya isa Maiduguri kai tsaye daga kasar Habasha bayan kammala taron kolin kungiyar tarayyar Afirka.

https://p.dw.com/p/3XgAJ
Muhammadu Buhari
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kai wata ziyarar ba zata a jihar Borno da ake ganin tana da nasaba da hare-haren da mayakan Boko Haram ke kaiwa a 'yan kwanakin nan musamman harin da suka kai garin Auno da mutane sama da 30 suka riga mu gidan gaskiya.

Shugaba Buhari wanda ya sauka a Maiduguri a wannan rana ta Laraba, kai tsaye daga kasar Habasha bayan kammala taron kolin kungiyar tarayyar Afirka, ya samu tarba daga gwamnan jihar Borno, inda suka yi ganawar sirri kafafin ayarin shugaban ya nufi cikin garin Auno.

Wakilinmu a Maiduguri Al-Amin Suleiman Muhammad ya ce babu tabbacin wuraren da shugaban zai ziyarta, sai dai jama'a na fatan ya je Auno ya ganewa kansa abin da ya faru da kuma ziyartar sansanonin 'yan gudun hijira.