1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Francois Hollande zai ƙara ƙwarin gwiwa ga sojojin Faransa a Mali

February 2, 2013

A ziyarar' da ya ke shirin kai wa a Mali ´a ,makonnin na ukku a faɗan da ake ci gaba da gwabzawa tsakanin dakarun ƙawancce da na masu kishin addini

https://p.dw.com/p/17Wvo
GettyImages 159874477 French President Francois Hollande delivers a speech during a joint session of the French National Assembly and the Bundestag at the German lower house of Parliament Bundestag on January 22, 2013 in Berlin, as part of the celebration to mark 50 years since the Elysee Treaty launched after WWII French-German cooperation. In signing the landmark treaty on January 22, 1963, then French president Charles de Gaulle and West German chancellor Konrad Adenauer sealed a new era of reconciliation between the former foes which has since driven European unity. AFP PHOTO / ODD ANDERSEN (Photo credit should read ODD ANDERSEN/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Nan gaba a yau a aka shirya shugaban ƙasar Faransa Francois Hollande zai kai ziyara a ƙasar Mali.Da farko dai shugaban zai isa a garin Sevare inda shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya na Mali Dioncounda Traore zai tarbe shi .kafin daga bisani su isa a garin Timbuktu mai daɗanɗan tarihi da ke a yankin arewancin ƙasar.

Inda aka shirya zai gana da sojojin Faransa da na Mali sannan ya ziyarci gidan addana kayan tarihi da masu kishin addinin suka ƙona,ana sa ran shugaban Francois Hollande zai yi kira ga ƙasashen Afirka da su ƙara ba da hima wajan kawo ɗauki.bayan makonnin ukku na faɗan da ake yi wanda a kan sa dakarun Faransa suka sake ƙwacce kusan dukanin yankunan da yan ta'adar suka mammaye sannan kuma ana sa ran wata ƙila zai tattauna batun maye gurbin dakarun Faransa da na Afirka.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita :Usman Shehu Usman