1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Afirka ta Kudu zai bayyana a gaban majalisa

Salissou BoukariFebruary 11, 2016

Shugaba Jacob Zuma, zai yi jawabinsa na shekara-shekara a gaban majalisar dokokin kasar, a daidai lokacin da ya ke fuskantar matsin lamba daga 'yan adawa.

https://p.dw.com/p/1Hteh
Jacob Zuma
Jacob ZumaHoto: Reuters/N. Bothma

'Yan adawar kasar ta Afirka ta kudu dai, na nema da Shugaban Zuma ya yi murabus sakamakon badakalar da ta taso kan batun gina wani katafaran gidansa mai na Nkandla da kudadan al'ummar kasar. Baya ma ga wannan batu, akwai kuma batun matsalar tattalin arzikin kasar wanda ake ci gaba da gani bayan korar ministocin kudin kasar har guda biyu da shugaban ya yi a watan Disamba da ya gabata.

Tuni dai jam'iyyar adawa ta EFF ta Julius Malema, ta sha alwashin tada tarzoma ya yin jawabin na shugaba Zuma muddin dai shugaban bai ba su haske ba kan batun korar mistocin kudin da ya haddasa faduwar darajar kudin kasar.