1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban gwamnatin Burkina Faso ya koma madafun iko

Suleiman BabayoSeptember 24, 2015

Bayan matsin lamba daga kasashen duniya sojojin da suka yi juyin mulki a Burkina Faso sun ajiye madafun iko inda aka sake mayar da gwamnatin rikon kwarya.

https://p.dw.com/p/1GcET
Burkina Faso neue Regierung in Ouagadougou Gruppenfoto
Hoto: STR/AFP/Getty Images

Shugaban gwamnatin wucin gadi na kasar Burkina Faso Michel Kafando ya koma kan madafun iko a wannan Laraba da ta gabata, yayin wani karamin biki, mako guda bayan juyin mulkin da sojoji suka yi, wadanda suke da dangantaka da tsohon Shugaba Blaise Compaore.

Jagoran juyin mulkin Janar Gilbert Diendere ya nemi gafara, kuma ya amince da kusruren da ya yi na kifar da gwamnati abin da ya janyo tir daga ciki da wajen kasar. Sojojin kasar ta Burkina Faso da suka jagoranci juyin mulkin sun fuskanci matsin lamba daga kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yankin yammacin Afirka, ECOWAS, da kuma Faransa wadda ta yi wa kasar mulkin mallaka da sauran kasashen duniya. Tuni Shugaba Kafando ya mayar da gwamnati karkashin Firaminisa Isaac Zida.