Shugaban Hisbollah ya ce ana tattaunawa da Isra´ila
November 1, 2006Talla
Shugaban Hisbollah Sayyed Hassan Nasrallah ya ce an fara wata tattaunawa tsakanin kungiyarsa da Isra´ila ta hanyar wani mai shiga tsakani na MDD don yin musayar firsinoni. A lokacin da yake magana ta tashar telebijin din kungiyar Hisbollah Nasrallah ya ce ana gudanar da wata tattaunawa ta gaske da wani wakilin MDD da bai bayanna sunansa ba. A ranar 12 ga watan yuli Hisbollah ta yi garkuwa da sojojin Isra´ila biyu a wani hari da suka kai kan iyaka. Hakan ya haddasa yakin kwanaki 34 da aka gwabza tsakaninta da rundunar Isra´ila a kudancin Libanon. Kawo yanzu Isra´ila ba ta ce uffan ba game da kalaman na Nasrallah.