1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban kasar Benin ya rusa gwamnati

August 9, 2013

Dr Thomas Yayi Boni ya kuduri aniyar girka sabuwar Majalisar Ministoci da za ta dukufa aikin kasa

https://p.dw.com/p/19NG4
Benin President Thomas Boni Yayi gives a press conference on October 26, 2012 after the signing of a convention between the European Union and Benin at the presidential palace in Cotonou. EU commission president Jose Manuel Barroso, who spoke alongside Yayi, said on October 26 that the European Union was working to establish a credible army in Mali, where radical Islamists took control of the north after a military coup. European leaders have vowed to back a proposed African force that may be sent to flush out the Islamists, but have said their support will not include EU combat troops. AFP PHOTO / KAMBOU SIA (Photo credit should read KAMBOU SIA/AFP/Getty Images)
Thomas Yayi BoniHoto: K.Sia/AFP/Getty Images

Shugaban Jamhuriyar Benin Dr Thomas Yayi Boni ya rusa gwamantinsa.

Kamfanin dullancin labarun Reuters da ya ruwaito wannan labari, ya ce sanarwar da fadar shugaban ta baiyana, ta ce Dr Yayi Boni, ya dauki wannan mataki, domin sabinta Majalisar Ministoci, wadda ya girka shekaru biyu kenan da suka gabata, lokacin da aka zabe shi a wa'adin mulki na biyu.

Russasar gwamnatin, ta kunshi ministoci 26, wanda ake zargin cewa sun fara hukewa, wajen gudanar da aiyukan kasa.

A cikin mako mai zuwa, ake sa ran shugaban kasar Benin, zai kafa sabuwar gwamnati.

Jamhuriyar Benin na daya daga kasashen Afirka kalilan, da suka fara cin gajiyar mulkin demokradiyar da aka kafa a shekara 1990.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Usman Shehu Usman