1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban kasar Burundi ya yi rantsuwar kama aiki

Salissou BoukariAugust 20, 2015

Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza, ya yi rantsuwar kama aiki a wannan Alhamis din a gaban kotun tsarin mulkin, da kuma 'yan majalisun dokokin kasar.

https://p.dw.com/p/1GIfl
Pierre Nkurunziza
Pierre NkurunzizaHoto: picture-alliance/dpa/C. Karaba

An rantsar da shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza a wani sabon wa'adi na uku, bayan da ya lashe zaben da aka gudanar a kasar mai cike da cece-kuce zaben da 'yan adawar kasar suka kaurace masa. An rantsar da shugaban na Burundi ne ya yin wani kware-kwaran biki da aka shirya a takaitaccen lokaci bisa dalillai na tsaro, wanda kuma kasashen duniya basu halarta ba. Kamar dai yadda dokokin kasar suka tanada, an rantsar da shugaban ne a gaban kotun tsarin mulkin kasar, da kuma 'yan majalisun dokokin kasar inda ya yi rantsuwar yin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasar, tare da hada kan 'yan kasar da a halin yanzu take fama da tashe-tashen hankulla.