1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Mauritaniya ya koma gida

November 25, 2012

Dubban mutane sun fito titunan Nouakchott babban birnin ƙasar Mauritaniya, domin tarbar Shugaba Ould Abdel Aziz

https://p.dw.com/p/16pSG
Hoto: AP

Dubban mutane sun fito titunan Nouakchott babban birnin ƙasar Mauritaniya, domin tarbar Shugaba Mohamed Ould Abdel Aziz, wanda ya yi jinya a asibitin ƙasar Faransa, bayan harbinsa bisa kuskure da wani jami'in tsaro ya yi.

Mutanen sun yi dafifi tun daga filin saukar jiragen sama zuwa cikin birnin, saboda maraba wa shugaban, wanda ya kwashe makonni shida yana jinya.

Shugaban ya koma gida ranar Asabar, 24.11.2012- abun da ya kawo ƙarshen jita-jitar game da lafiyar shugaba Abdel Aziz ɗan shekaru 55 da haihuwa.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita:Halima Balaraba Abbas