1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta nuna taka tsantsan sasantawa da Boko Haram

Suleiman BabayoSeptember 16, 2015

Shugaban Najeriya ya jaddada shirin gwamnatinsa na tattauna kan sako 'yan matan da ake garkuwa da su.

https://p.dw.com/p/1GXXT
Paris Medef Zentrale Buhari Gattaz
Hoto: Getty Images/AFP/E. Piermont

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya wanda yake kammala ziyarar aiki a kasar Faransa ya kara jaddada shirin gwamnatin kasar na tattauna da Boko Haram kan yadda za a sake 'yan mata 'yan makaranta na Chibok da tsagerun kungiyar suke garkuwa da su fiye da shekara guda da ta gabata. Kalaman shugaban na zuwa yayin da dakarun kasar ke samun nasara a yaki da tsagerun na kungiyar ta Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar.

A cikin hira da tashar talabijin ta Faransa Shugaba Buhari ya ce duk wata tattauna tilas a tantance wadanda za su wakilci kungiyar:

"Haka yana kara zama mai wahala, dole mu tantance wadanda suke ikirarin shugabancin Boko Haram, shin shugabannin ne na gaskiya kuma yaya tasirinsu a cikin kungiyar. Kuma sun san inda 'yan mata suke da halin da suke ciki. Amma kawai kowani dan kungiyar Boko Haram ya nemi gwamnati domin cewa shi shugaba ne da zai iya sako 'yan matan, dole mu yi taka tsantsan a kai."

A wannan Laraba Shugaban na Najeriya ya kammala ziyarar aikin a kasar ta Faransa.