1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Sudan ya bayyana shirin sakin fursunonin siyasa

April 1, 2013

'Yan adawa a ƙasar Sudan sun yi maraba sanarwar shugaban Omar al-Bashir, inda ya bayyana shirin sakin ɗaukacin fursunonin siyasa da ke tsare

https://p.dw.com/p/187om
!!! Zu Steffe, Sicherheitsrat verurteilt Überfall in Darfur - Sudan bestreitet Anschlag auf UN-Konvoi !!! Sudanese President Omar al-Bashir attends a peace rally in the capital, Khartoum, Tuesday, Jan. 8, 2008. The Sudanese army has attacked a convoy of United Nations peacekeepers in Darfur, critically injuring a driver, barely a week into their new mission in the wartorn region, the U.N. said Tuesday. The U.N. condemned the attack, which occurred late Monday, and said it had protested to the Sudanese government. (AP Photo/Alfred de Montesquiou)
Shugaban ƙasar Sudan Omar al-BashirHoto: AP

Shugaban gamayyan jam'iyyun adawan kasar ta Sudan guda 20, Farouk Abu Issa ya ce, wannan gagarumin mataki ne na tattauanawa da kawo ci gaba.

Shugaban kasar ta Sudan Omar al-Bashir ya bayyana shirin sakin daukacin fursunonin siyasa, matakin da 'yan adawa su ka yi lale-maraba da shi, wannan yayin da kasar ta rage zaman tankiya da makwabciyarta Sudan ta Kudu.

Lokacin jawabin bude zaman majalisar dokoki da ke birnin Khartoum, shugaban ya ce, za a saki daukacin fursunonin na siyasa ba tare da wani jinkiri ba, cikin matakan da ake dauka na sasantawa.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Usman Shehu Usman