1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi jana'izar tsohon magatakardan Majalisar Dinkin Duniya

Zulaiha Abubakar
September 13, 2018

Manyan shugabannin duniya sun halarci jana'izar tsohon magatakardar Majalisar Dinkin Duniya Kofi Annan a wannan Alhamis a kasar Ghana.

https://p.dw.com/p/34oJ1
Kofi Annan ist verstorben
Hoto: Reuters/D. Balibouse

Marigayin dan asalin birnin Kumasi na yankin Ashanti dake kudancin kasar ta Ghana, ya sadaukar da rayuwar sa wajen hidimta wa al'umma a Majalisar Dinkin Duniya. Jim kadan bayan binne shi, matarsa Nane Maria ta bayyana shi a matsayin Gwarzo mai juriyar da za a jima ba a mayar da madadin sa ba.

Za a cigaba da tuna marigayin a matsayin bakar fata na farko da ya rike wannan mukami tsakanin shekarar 1997 zuwa 2006. Annan ya rasu ranar 18 ga watan Agusta yana da shekaru 80, bayan gajeriyar jinya da ya yi a kasar Switzerland.