Sojoji na ci gaba da hare-hare a biranen kasar Cote d'Ivoir
May 15, 2017Talla
Wani mai magana da yawun sojojin da ke bori a birnin Abidjan ya sanar a wannan Litinin din cewa, tattare hanyoyi da suka yi, da kuma harbe-harben da suke yi ba juyin mulki ba ne, illa kawai nuna buktar su ta a biya su kudadansu kamar yadda shugaban kasar Alassane Ouattara ya rattaba hannun cewa zai biya su.
A ranar Alhamis ce dai da ta gabata wani mai magana da yawun sojojin da suka yi bori a kasar ya nemi gafara a gaban Shugaban kasar Alassane Ouattara dangane kan borin da suka yi a baya, inda kuma ya sanar cewa sun yi watsi da dukannin bukatunsu na neman a biya su wasu kudaden na alawus, sai dai kuma ga dukkan alamu wannan mataki bai yi wa saurau sojojin dadi ba.