1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Najeriya sun jikkata Shekau

Abdul-raheem HassanAugust 23, 2016

Rundunar Sojoji sun bayyana sunayen Abubakar Mubi da Malam Nuhu da Malam Hamman cikin manyan kwamandojin Kungiyar da aka hallaka a wannan hari.

https://p.dw.com/p/1JnJM
Nigeria Soldaten in Damboa
Hoto: Getty Images/AFP/S. Heunis

Rundunar sojojin Najeriya ta sanar da cewa hari da mayakan ta na sama suka kai a sansanin Boko Haram ya hallaka wasu jiga-jigan kungiyar, inda suka yi nasarar naskasa Abubakar Shekau da ke cikin masu ikirarin shugabantar kungiyar.

Sanarwa da kakakin rundunar Sojojin Kanar Sani Usman Kuka Sheka ya fitar a ranar Litinin, na cewa sun kaddamar da hare-hare ne a ranar Juma'ar da ta gabata a kauyen Taye dake yankin Gombale, inda aka jikkata wasu manyan kwamandojin kungiyar.

Sanarwar ta kuma bayyana sunayen Abubakar Mubi, da Malam Nuhu da Malam Hamman a cikin sanarwar, wan da ke nuna cewa mutanen na cikin manyan kwamandojin Kungiyar da aka hallaka a hari. Amma kawo yanzu babu wata kafa mai zaman kanta da ta tabbatar da ikirarin Sojojin, kazalika su ma kungiyar ba su ce komai kan sanarwar sojojin ba.

A baya dai Sojojin sun sha ikirarin cewa sun hallaka shugaba Kungiyar Abubakar Shekau sai dai Kungiyar kan musanta ta hanyar wallafa faifen bidiyo da shugaban ke raddi.