1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Najeriya sun kashe Abubakar Shekau

Abdourahamane HassaneSeptember 24, 2014

A karon farko rundunar sojojin Najeriya ta tabbatar da hallaka jagoran Boko Haram Abubakar Shekau.

https://p.dw.com/p/1DKcb
Boko-Haram-Chef Abubakar Shekau BITTE BESCHREIBUNG BEACHTEN / SCHLECHTE QUALITÄT
Hoto: picture-alliance/dpa

Rundunar ta sanar da cewar sojojin sun samun gawar mutumin da ke zaman jagoran masu tada ƙayar bayan.Kakakin sojin Najeriyar Manjo Janar Chris Olukolade ya shaida wa manema labarai a birnin Abuja cewar,An kashe Mohammed Bashir yayin fafatawar da aka yi a garin Konduga na Jihar Borno da ke a yanki arewa maso gabashin ƙasar.

Kuma ya ce shi ne yake fitowa a faifan bidiyo a matsayin jagoran ƙungiyar,wato Abubakar Shekau wanda aka daɗe da kashewa.