1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojoji na kashe farar hula a Sudan

Abdourahamane Hassane
January 14, 2019

Kungiyar tarrayar Turai ta ce tana da bayanai da ke tabbatar da cewar jami'an tsaro na bude wuta da gaske ga masu yin zanga-zangar neman sauyi a Sudan.

https://p.dw.com/p/3BV09
Sudan Demonstrationen Proteste
Hoto: Reuters/M. N. Abdallah

Kungiyar ta EU ta ce shaidu sun bayyana cewar 'yan sandar na bin jama'ar a kan tituna har ma cikin gidaje suna fatatakarsu, wasu rahotannin da aka bayyana sun ce jami'an tsaro har ckin asibiti suke kai hare-haren a zanga-zanga da kungiyoyin suka kira a karshen mako. Kungiyar kare hakin bil Adama ta Human Rights Watch ta ce an kashe mutane kusan 40 a zanga-zangar ta neman shugaba Omar al-Bashir  ya yi marabus, sai dai gwamnatin ta ce mutane 24 kawai suka mutu.