1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsugune bata kare ba a Sudan

Zainab Mohammed Abubakar
May 11, 2019

Wata guda bayan kifar da gwamnatin Al-Bashir na Sudan, babu alamun sojojin kasar zasu mika mulki wa farar hula, a daya hannun kuma tattaunawa tsakanin kungiyoyi da majalisar mulkin sojin ta rushe

https://p.dw.com/p/3ILLJ
Sudan Khartum Proteste am Militärhauptquartier
Hoto: Getty Images/AFP/A. Shazly


Dubban masu zanga-zanga nedai suka kafa sansaninsu a wajen ginin headkwatar rundunar soji da ke tsakiyar birnin Khartoum, inda suka lashi takobin tursasawa shugaban mulkin sojin yin murabus, kamar yadda suka tusa keyar Al-Bashir.

Al'ummar Sudan din a cewar daya daga cikin masu zanga zangar  zaman dirshan din mai sunaIman Hussein, sai sun ga abunda ya turewa buzu nadi dangane da kafuwar gwamnatin farar hula, wanda suka fara tun ranar 6 ga watan Afrilu.

Da farko dai gangamin na korar Al-Bashir ne, yanzu kuma ya rikide zuwa na korar wadanda suka taimaka wajen kifar da Al-Bashir din a ranar 11 ga watan Afrilu.