1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan ta Kudu: An sako ma'aikatan agaji da aka sace

Abdul-raheem Hassan
April 30, 2018

'Yan bindiga sun sako ma'aikatan agaji 10 na kungiyar Red Cross da aka yi garkuwa da su makon jiya a kudancin Sudan ta Kudu.

https://p.dw.com/p/2wwPp
Rot-Kreuz-Hilfslieferung für Darfur
Hoto: picture-alliance/dpa

Wannan dai ba shi ne karon farko da ma'aikatan agaji ke fuskantar barazanar kai hare-hare a yankunan da ke fama da tashe-tashen hankula a Sudan ta Kudu ba. Majalisar Dinkin Duniya ta ce rikicin kasar ya lamushe rayukan ma'aikatan agaji 100 tun watan Disamban shekara ta 2013, a yanzu dai tuni aka wuce da ma'akatan da sukia kubuta a jitgin Red Cross zuwa Juba babban birnin kasar Sudan ta Kudu.