1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Syriya na neman a dakatar da buɗe wuta

Jane McintoshSeptember 20, 2013

Mataimakin firaminista na Syriya Qadri Jamil ya bayyana cikin wata hira da jaridar The Guardian cewa a shirye gwamnatinsa ta ke ta tsagaita bude wa 'yan tawaye wuta.

https://p.dw.com/p/19kw1
Bildnummer: 53597345 Datum: 13.11.2009 Copyright: imago/UPI Photo Syrian President Bashar al-Assad speaks to journalists after his meeting with French President at the Elysee Palace, in Paris, November 13, 2008. PUBLICATIONxINxGERxSUIxAUTxHUNxONLY People Politik Staatsbesuch Porträt kbdig xmk 2009 quer Bildnummer 53597345 Date 13 11 2009 Copyright Imago UPi Photo Syrian President Bashar Al Assad Speaks to Journalists After His Meeting With French President AT The Elysee Palace in Paris November 13 2008 PUBLICATIONxINxGERxSUIxAUTxHUNxONLY Celebrities politics State Visit Portrait Kbdig xmk 2009 horizontal
Hoto: imago/UPI Photo

Syriya ta yi gargaɗin cewar a shirye ta ke ta nemi a kawo ƙarshen yaƙin da ta ke yi da' yan tawaye a gaban taron ƙasa da ƙasa da za a yi a birnin Jeniva . Wani babban jami'in gwamnatin Qadri Jamil shi ne ya bayyana haka a lokacin wata tattaunawa da jaridar The Guardian.

Jamil ya ce a akwai buƙatar a dakatar da yaƙin saboda daga dukkanin ɓangarorin biyu babu wani wanda ke da ƙarfin samun nasara a faɗan. Mutane dai kusan dubu ɗari ne suka rasa rayukansu a yaƙin na Syriya,kuma ministan ya ce ya zuwa yanzu sun kashe kuɗaɗe sama da miliyan dubu ɗari saboda yaƙin.

Mawallafi :Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe