1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takaddama a kan gwamnatin kawance a Nijar

August 17, 2013

Jam'iyyar Moden Lumana Afrika ta bayyana ficewarta daga gwamantin hadin kasa ta Jamhuriyar Nijar.

https://p.dw.com/p/19RbB
epa02847783 President Mahamadou Issoufou of Niger during a meeting with US President Barack Obama and fellow African leaders from Niger, Benin, and Guinea, in the Cabinet Room of the White House, in Washington DC, USA, 29 July 2011. EPA/MARTIN H. SIMON / POOL +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture alliance / dpa

Jam'iyyar Moden Lumana Afrika ta shugaban majalisar dokokin Jamhuriyar Nijar Hama Amadou, wadda ke kawance da jam'iyyar shugaba Muhammadu Isuhu, wato PNDS Tarayya, ta bada sanarwar dakatar da ministocinta daga cikin sabuwar gwamnatin hadin kan kasa da shugaban kasar ya kafa a farko-farkon wannan makon.

Jam'iyyar ta ce ta dau wannan mataki ne saboda rashin amincewarta da kason da aka bata a cikin sabuwar majalisar ministocin kasar sai dai jam'iyyar ta ce za ta cigaba da kasancewaa cikin kawancen jam'iyyun da ke milki a kasar.

Mawallafi : Gazali Abdou Tasawa
Edita : Saleh Umar Saleh