1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Armeniya da dangantakar Jamus da Turkiya

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 1, 2016

Gabanin majalisar dokokin Jamus ta amince da kudiri kan batun kisan kiyashi na Armeniyawa, Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiya ya gargadi Jamus din da kada ta kuskura ta zartas da kudirin.

https://p.dw.com/p/1Iy62
Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan
Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da shugaban Turkiya Recep Tayyip ErdoganHoto: picture-alliance/dpa/K. Nietfeld

Wannan kudiri dai in har majalisar dokokin ta Jamus ta amince da shi, zai nunar da cewa Turkiyan ta aikata kisan kiyashi a kan Armeniyawa, a yayin yakin duniya na farko da aka yi a shekara ta 1915. Erdogan dai ya yi gargadin ne yayin wata tattaunawa da suka yi da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta wayar tarho, inda ya ce in har majalisar dokokin Jamus din ta yi gigin amincewa da wannan kudiri, to tabbas a shirye Turkiya take ta yanke duk wata hulda ta siyasa da tattalin arziki da ma ta soji tsakaninta da Jamus din. Turkiya dai ta dage kan cewa babu wani batun kisan kiyashi, kana yawan mutanen da suka rasa rayukansu a wannan lokaci bai wuce 500,000. Sai dai a hannu guda Jamus na cewa adadin mutanen da suka rasa rayukansu a yayin yakin duniya na dayan, sun kai miliyan guda da rabi. Wannan batu dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da Jamus ke bukatar taimakon Turkiya kan batun kwararar 'yan gudun hijira zuwa Turai da mafi yawa daga cikin su ke son shiga Jamus.