1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

Jamus ta nemi ganin mafita tsakanin Amirka da China

Suleiman Babayo MAB
June 28, 2019

Ganawa tsakanin shugaban Amirka da na China gami da kasuwanci tsakanin kasashen ya dauki hankalin taron G20 da ke gudana a Japan.

https://p.dw.com/p/3LGtF
Japan Osaka | G20 Gipfel | Joko Widodo | Moon Jae-in
Hoto: President Secretary/Laily Rachev


Batun harkokin kasuwanci na ci gaba da samun tagomashi a taron manyan kasashe da ke sahun gaba wajen karfin tattalin arziki a duniya na G20 da ke gudana a kasar Japan. Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel tana fata za a samun mafita kan kiki-kaka tsakanin kasashen Amirka da China wadanda suke gaban gaba wajen karfin tattalin arziki a duniya. Yayin da ake shirin ganawa tsakanin Shugaba Donald Trump na Amirka da takwaransa Xi Jinping na China a gefen taron.

Haka kungiyar kasashen Tarayyar Turai suna tattauna samun kasuwanci ba shinge da kasashen kudancin Amirka. Ana samun dari-dari a kasuwar hannun jari a duniya saboda rashin tabbas na abubuwa da za a cimma a wannan taro na G20 da ke gudana a kasar Japan.