1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Afirka da EU a birnin Abidjan

Mohammad Nasiru Awal SB
November 29, 2017

Shugabannin Afirka da na kungiyar EU fiye da 80 sun hallara a birnin Abidjan don gudanar da taron hadin gwiwa don duba bukatun Afirka.

https://p.dw.com/p/2oTKC
EU-Afrika-Gipfel Bundeskanzlerin Angela Merkel und Alassane Ouattara
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler

Fiye da shugabanni 80 na kasashen Afirka da Tarayyar Turai sun hallara a birnin Abidjan na kasar Cote d'Ivoire inda za su gudanar da wani taron hadin gwiwa da ke da nufin kirkiro guraben aikin yi da tabbatar da kwanciyar hankali a nahiyar Afirka mai samun bunkasar al'umma fiye da kima.

Wasu na kira da a kirkiro da sabon shirin Marshall Plan, shigen wanda aka yi amfani da shi aka tallafa wa Jamus bayan yakin duniya na biyu.

Taron na yini biyu da ake budewa a wannan Laraba ya zo ne yayin da kungiyar Tarayyar Turai EU ta farga cewa makomarta na da alaka da yawan bakin haure da ke gudu daga Afirka zuwa Turai da kuma batun hare-haren 'yan ta'adda.

Taron ya kuma zo ne a daidai lokacin da kasashen China da Indiya da Japan da kasashen yankin Gulf ke gogayyar samun angizo a nahiyar Afirka, inda har yanzu kungiyar EU ta kasance babbar mai taka rawa a fannin tattalin arziki da siyasa.