1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron kolin kasashen Euromed na fuskantar barazanar watsewa

November 27, 2005
https://p.dw.com/p/BvJ6

Ana fuskantar barazanar tashi baram-baram a taron kolin kasashen tarayyar Turai EU da takwarorinsu na yankin tekun Bahar Rum saboda takaddama akan ma´anar ta´addanci. Yayin da kungiyar EU ke son ta yi suka da kakkausar harshe akan ayyukan ta´addanci, su kuwa wakilan kasashen Larabawa na son a mayar da hankali ne akan Falasdinawa musamman dangane da ´yancin bijirewa matakan mamaya. Ga sabuwar shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel wannan taron wanda za´a fara da yammacin yau a birnin Barcelona zai kasance taron koli na farko da za ta halarta a waje tun bayan darewarta kan kujerar shugabar gwamnatin kasar ta Jamus a ranar talata da ta gabata. Merkel zata gana da FM Spain Jose Luis Rodrigues Zapatero da kuma FM Turkiya Recep Tayyip Erdogan.