1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tattaunar samar da zaman lafiya

September 2, 2010

Isra'ila da Palasɗinu sun jadada buƙatar samar da masalha akan rikicin da ake fama da shi a yanki gabas ta Tsakiya

https://p.dw.com/p/P2x6
Hoto: picture-alliance/dpa

Fraministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce a shirye ƙasarsa ta ke ta yi na'am da shirin zaman lafiyar da za a cimma domin kawo ƙarshen kaka gidan da Ira'ila ke yiwa Palasɗinu.Shugaban Palasɗiniyawan dai Mahamou Abbas ya ce wajibine Isra'ila ta amince da dakatar da gina matsugunan yahudawa kwata kwata.

da ta ke magana ga shugabannin biyu sakatariyar harkokin wajen Amurka Hilary Clinton ta yi gargaɗin cewa taron da ake yi zai iya kawo canji ga makomar al'umomin yankunan biyusanan kuma ta ci-gaba da cewa

Ta c e ina sane da cewar ba ƙaramin aiki ne ba shawara da za a cimma a wannan tebrin shawarwari, to amma ganin yada har ku ka amince a tattauna wannan wani baban ci-gaba da ke ciki da tarihi ga wannan rikici da aka ƙwashe shekaru ana yi kuma ina jinjinamaku akan wannan kokari.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane

Edita : Umaru Aliyu